Home / Art / Hausa al'adu / ‘Yan Fashin Sun Kashe ‘Yan Sanda Biyu Tare Da Raunata Guda Uku A Yayin Da Suka Kaiwa Wata Motar Banki Farmaki
money van

‘Yan Fashin Sun Kashe ‘Yan Sanda Biyu Tare Da Raunata Guda Uku A Yayin Da Suka Kaiwa Wata Motar Banki Farmaki

Wasu gaggan ‘yan fashi sun kashe jami’an ‘yan sanda guda biyu tare da raunata guda uku, a yayin da suka kaiwa wata mota mallakar babban bankin kasa farmaki a daidai tsaunin Hawan Kibo dake kusa da garin Riyom a jihar Filato.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Terna Tyopev ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai cewa ‘yan fashin sun kaiwa motar farmaki ne, inda uku daga cikin ‘yan sandan da suka rako motar suka samu rauni.

 
Motar dai tana dauke ne da kudi inda ta taho daga garin Jos za ta je garin Lafiya babban birnin jihar Nassarawa.
Saidai kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa barayin ba su yi sa’ar tafiya da kudin ba kasancewar jami’an sun yi gaggawar daukar mataki. Sannan kuma suna kan ci gaba da gudanar da bincike domin gano barayin.

 

Rariya

About AbubakarMuhd

VI

Viral Video

Support Ooduarere

SUPPORT OODUARERE
Scan QR code below to Donate Bitcoin to Ooduarere
Bitcoin address:
1FN2hvx5tGG7PisyzzDoypdX37TeWa9uwb
x

Check Also

The Hidden History of Hausa Enslavement Under the Sokoto Caliphate

The Hidden History of Hausa Enslavement Under the Sokoto Caliphate

I have looked into the historical records written by scholars about the Sokoto Caliphate. And I have discovered a great and harsh truth. The truth is that after Usman dan Fodio and his Fulani warriors seized the Hausa kingdoms, they turned the Hausa people into slaves. This was not an accident or a mistake. This was a carefully planned system. Its purpose was to destroy the dignity of the Hausa people, to remove them from power, and to force them ...