Home / Art / Hausa al'adu / Rikicin Majalisa Kan Aringizon Kasafin Kudi Na Kara Ta’azzara
senate

Rikicin Majalisa Kan Aringizon Kasafin Kudi Na Kara Ta’azzara

Rikicin majalisar wakilai kan badakalar aringizon kasafin kudi na kara ta’azzara bayan da majalisar ta gayyato hukumar EFCC kan ta tuhumi tsohon shugaban kwamitin kudi na majalisar, Jibrin Abdulmumini wanda ya fallasa batun aringizon.

 
Majalisar dai na son EFCC ta fara binciken Hon. Jibrin ne tun daga lokacin da yake shugaban kwamitin kudi na majalisa a tsakanin shekarun 2011 zuwa 2014 inda suke zargin ya fice wajen aringizon kasafin kudi ta yadda har sai da ya sanya tsohon Shugaban majalisar, Aminu Tambuwal kuka.

 
Wata majiya daga majalisar ta nuna cewa tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya hana Tambuwal daukar matakin ladaftarwa a kan Hon. Jibrin. Shugaban kwamitin majalisar kan Yada labarai, Hon. Abdulrazak Namdas ya tabbatar da cewa majalisar za ta ladaftar da Hon. Jibrin kan wannan zargi da ya gabatar a akan shugabannin majalisar.

Cc-Rariya

About AbubakarMuhd

Viral Video

Support Ooduarere

SUPPORT OODUARERE
Scan QR code below to Donate Bitcoin to Ooduarere
Bitcoin address:
1FN2hvx5tGG7PisyzzDoypdX37TeWa9uwb
x

Check Also

found

Cigiyar Iyayen Yaron Da ‘yan Sandan Jihar Taraba Suka Kubutar Da Shi

Daga Shafin Biyora Adamu Aliyu Dan shekara Goma sha biyu daga unguwar Na’ibawa ‘Yan Lemo Kano jami’an ‘yan sanda a jihar Taraba sun sami nasarar kubutar da shi. Idan ‘yan uwansa sun gani ko wanda ya san shi sai ya tuntubi hukumar ‘yan sanda ta jihar Taraba. Gani nayi a Facebook na kwafo….. bani da masaniya akan lamarin… nayi ne kawai ko Allah zaisa ‘yan uwansa su gani a posting dina…..